2 Peter 1

1Wasiƙa daga Siman Bitrus, bawa da kuma manzon Yesu Kiristi.

Zuwa ga waɗanda ta wurin adalcin Allahnmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi sun sami bangaskiya mai daraja irin tamu:

2Alheri da salama su zama naku a yalwace ta wurin sanin Allah da Yesu Ubangijinmu.

Mai da Kira da kuma Zaɓen Da aka wa Mutum Yǎ Zama Tabbatacce

3Ikonsa na Allahntaka ya ba mu kome da muke bukata don rayuwa da kuma tsoron Allah ta wurin sanin wanda ya kira mu ta wurin ɗaukakarsa da nagartarsa. 4Ta wurin waɗannan ya ba mu alkawaransa masu girma da kuma masu daraja, domin ta wurinsu ku iya yin tarayya cikin Allahntakarsa, ku kuma kuɓuta daga lalatar da take cikin duniya wadda mugayen shaʼawace-shaʼawace suke jawowa.

5Saboda haka, ku yi iyakar ƙoƙari ku ƙara wa bangaskiyarku nagarta; ga nagarta kuwa, ku ƙara mata sani; 6ga sani kuma ku ƙara masa kamunkai; ga kamunkai kuma ku ƙara masa ɗaurewa; ga ɗaurewa kuwa ku ƙara mata tsoron Allah; 7ga tsoron Allah kuma ku ƙara masa nuna alheri ga ʼyanʼuwa; ga nuna alheri ga ʼyanʼuwa kuma ku ƙara masa ƙauna. 8Domin in kuna ƙaruwa a waɗannan halaye, za su kāre ku daga rashin tasiri da rayuwa na rashin amfani cikin saninku na Ubangijinmu Yesu Kiristi. 9Amma in wani ba shi da su, ba shi da hangen nesa ke nan kuma makaho ne, ya kuma manta cewa an tsarkake shi daga zunubansa na dā.

10Saboda haka ʼyanʼuwana, ku ƙara aniya wajen tabbatar da kiranku da zaɓenku da aka yi. Gama in kuka yi waɗannan abubuwa, ba za ku taɓa fāɗuwa ba, 11za ku sami kyakkyawar marabta cikin madawwamin mulkin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi.

Annabcin Nassi

12Saboda haka kullum zan tuna muku da waɗannan, ko da yake kun sansu kun kuma kahu ƙwarai cikin gaskiyar da kuke da ita yanzu. 13A ganina ya dace in tunashe ku muddin ina raye cikin tentin wannan jiki, 14domin na sani na kusa in ajiye shi a gefe, yadda Ubangijinmu Yesu Kiristi ya nuna mini a sarari. 15Zan kuwa yi iyakacin ƙoƙari in ga cewa bayan rabuwata kullum za ku iya tuna da waɗannan abubuwa.

16Ba mu bi tatsuniyoyin da aka ƙaga da wayo saʼad da muka gaya muku game da ikon Ubangijinmu Yesu Kiristi da zuwansa ba, sai dai mu shaidu ne na ɗaukakarsa mai girma da muka gani da ido. 17Gama ya sami girma da ɗaukaka daga Allah Uba saʼad da murya ta zo masa daga Mafificiyar Ɗaukaka, cewa, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; da shi nake jin daɗi ƙwarai.”
Mat 17.5; Mar 9.7; Luk 9.35
18Mu kanmu mun ji wannan muryar da ta zo daga sama saʼad da muke tare da shi a kan dutse mai tsarki.

19Muna kuwa da maganar annabawa da aka ƙara tabbatar mana, zai fi kyau in kuka lura da ita, kamar hasken da yake haskakawa a wuri mai duhu, har yǎ zuwa wayewar gari da kuma haskakawar tauraron asubahi a zukatanku. 20Gaba da kome dai, dole ku gane cewa babu annabcin Nassin da ya fito daga fassarar annabi da kansa. 21Gama annabci bai taɓa samo tushensa daga nufin mutum ba, sai dai mutane sun yi magana daga Allah yayinda Ruhu Mai Tsarki ya bishe su.

Copyright information for HauSRK